Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kiran Zaman Lafiya Ga ‘Yan Siyasa Lokacin Zaben Nijar


Jamhuriyar Nijar: Hotom Madam Bayard ta hukumar zabe
Jamhuriyar Nijar: Hotom Madam Bayard ta hukumar zabe

Yanzu haka dai garin damagaran ya dauki harama tun da aka gudanar da yakin neman zabe a hukumance, komai ya kankama inda jam’iyyu suka lika fastoci da kyallaye a tituna da jikin motocinsu.

‘yan siyasa na ta ganawa da magoya bayan su a birane da karkara, don kaucewa duk wani tashin hankali ko rigingimu ‘yan siyasa sun kira magoya bayansu da su gujewa haddasa fituna ko tsokana, kamar yadda Bazu Muhammed na jam’iyyar PNDS Tarayya yayi kiran.

Shima Abdul Majid na jam’iyyar Hakuri, cewa yayi magoya bayansu su bi doka, ya kuma ci gaba da cewa tunda suka fito daga kotu sun ci gaba da nuna halin ‘da’a da juriya da hakuri da biyayya.

Sha’aibu Musa babban mai shari’u a kotun Damagaran, ya ja hankalin ‘yan siyasa da magoya bayansu da su kiyaye doka da oda.

Saurari cikakken rahotan Tamar Abari.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG