Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu ta Mayar da Danladi Gwamnan Taraba


Danbaba Suntai.
Danbaba Suntai.

Kotun koli a birnin Tarayyar Najeriya Abuja, ta yanke hukuncin mayar da tubabben mataimakin gwamnan Jihar Taraba, Alhaji Sani Danladi a matsayin gwmanan Jihar.

A halin yanzu dai an girke jami’an tsaro a cikin birnin Jalingo domin gudun tada zaune-tsaye.

Cikin shirin ko-ta-kwana, domin gudun abunda ka iya faruwa, a birnin Jalingo bayan hukuncin da kotun kolin ta yanke Juma’arnan, inda ta bukaci a hanzarta rantsar da tsohon mataimakin gwamnan Jihar, Alhaji Sani Danladi da ‘yan majalisar dokokin jihar suka tsige a baya.

Barrista Solomon Dalung, na daga cikin lauyoyin da suka wakilci Alhaji Sai Danladi.

“Ainihin kwayar magana, itace a bi ka’ida, yanda tsarin mulki ya shimfida, idan tsige shi za’a yi. Abunda muka kalubalanta kennan”, inji Dalung.

Yanzu haka wannan hukunci ya raba hankulan al-ummar Jihar tsakanin masu murna, da wadanda ke takaici.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:02 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG