Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu ta umarci gwamnatin soji a hamhuriyar Niger ta saki tsohon shugaban kasar


Tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Niger Mamadou Tandja
Tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Niger Mamadou Tandja

Kotun kungiyar cinikayya da bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirka ta yamma ECOWAS, a zaman da tayi a birnin tarayyar Nigeria Abuja yau litinin,ta yanke hukunci tare da baiwa shugabannin mulkin sojin kasar Niger umarnin sakin tsohon shugaban kasar Mamadou Tandja da aka hambaras a juyin mulki.

Kotun kungiyar cinikayya da bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirka ta yamma ECOWAS, a zaman da tayi a birnin tarayyar Nigeria Abuja yau litinin, ta yanke hukunci tare da baiwa shugabannin mulkin sojin kasar Niger umarnin sakin tsohon shugaban kasar Mamadou Tandja da soja suka hambaras a juyin mulkin da suka aiwatar. A watan Fabarairu ne rundunar sojin jumhuriyar Nijer ta hambaras da Gwamnatin farar hula karkashin jagorancin Mr. Tandja, watanni shida bayan tilasta yin sauye-sauye a kundin tsarin mulkin jkasar domin bashi damar ci gaba da mulki. Shugabannin sojin da suka yi juyin mulkin sun yi alkawarin maida mulki ga farar hula bayan gudanar da zaben a watan Afrilu mai zuwa.

XS
SM
MD
LG