Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotun Kolin Kasar Kenya Ta Tabbatar Da Zaben Uhuru Kenyatta


Zaman Kotun Kolin Kasar Kenya
Zaman Kotun Kolin Kasar Kenya
Kotun kolin kasar Kenya ta yanke hukumci yau asabar inda ta tabbatar da sahihancin, sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar ranar 4 ga watan Maris da cewa Uhuru Kenyatta shine ya lashe zaben.

Hukumcin da kotun ta yanke yau ya biyo bayan karar da aka shigar kotu da ya tada hankalin kasar. Yanke wannan hukumcin na nuni da cewa, za a rantsar da Kenyatta watan gobe a matsayin shugaban kasa.

Hukumar zaben kasar Kenya tace Uhuru Kenyatta ya lashe zaben da sama da kashi hamsin bisa dari na kuri’u. sai dai abokin hamayyarsa Raila Odinga yace an sauya sakamakon wadansu mazabu.

Wadansu kungiyoyi kuma sun ce hukumar zaben ta sanar da sakamakon zabe tun kafin ta kamala kirga kuri’u.

Hukumcin da kotun kolin ta yanke cewa ba a bukatar gudanar da zagaye na biyu na zaben shugaban kasar zai kwantar da hankalin al’ummar kasar Kenya da suke fargaban yiwuwar shida tashin hankali.
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG