Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar ISIS Ta Kashe Wani Gwamna a Kasar Yamal


Motar gwamnan da bam ya tarwatsa
Motar gwamnan da bam ya tarwatsa

Kungiyar ta ISIS, ta dauki alhakin wani harin bam da ya kashe gwamnan Lardin Aden a kudancin kasar Yamal tare da wasu da yawa daga cikin masu tsaron lafiyarsa.

Harin ya kaikaci jerin gwanon motocin Gwamna Gaafar Mohammed Sa’ad ne, yayin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa ofis a birnin Aden a jiya Lahadi.

Birnin na Aden, ya kasance filin daga a kasar ta Yamal, inda ‘yan tawayen Houthi suka karbe ikon Sana’a a bara kafin su doshi Aden, inda suka tilastawa Shugaba Abd Rabbu Mansour Hadi yin hijra zuwa Saudiyya, wanda sai a watan da ya gabata ne koma garin.

Wannan fada na Yamal ya kashe dubban mutane, kuma mafi yawancinsu fararen hula, lamarin da ya sa Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana kasar a matsayin wacce al’umarta ta fada mawuyacin hali.

XS
SM
MD
LG