Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Ma'aikatan Kananan Hukumomin Najeriya ta Yi Taron Share Faggen Taron Kasa.


South Africa Sudan President
South Africa Sudan President

Yayin da ake shirin taron kasa kungiyar ma'aikatan kananan hukumomi taro ta yi na samun hadin kai yadda zasu kubutar da kananan hukumomi daga gwamnonin jihohi

Kungiyar Ma'akatan kananan hukumomi ta dade tana neman a fitar da kanan hukumomi daga mugun ikon da gwamnoni ke nunawa a kansu musamman kan nasu kason kudi daga gwamnatin tarayya.

Makasudin taron da suka shirya a yankin kudancin Najeriya shi ne domin zaburar da shugabannin kananan hukumomi 774 a kan yadda za'a yi adalci kan kudin hukumomin da kungiyarsu. Suna kuma son su wayar da kawunan shugabannin su tashi tsaye su kare mutunci kananan hukumomi da 'yancinsu da kuma kare ma'aikata. Suna son su yi anfani da taron kasa su samu abun da basu samu ba lokacin da majalisun tarayya suka yiwa kundun tsarin mulkin kasar garambawul.

A taron kasa suna son a tabbatar da 'yancin kananan hukumomi su koma karkashin mutanen karkara domin su ne ke da su. Lokaci ya zo da zasu tsayar da magana daya domin kare 'yancin kananan hukumomi. Hanya mafi a'ala kuma da za'a tabbatar da 'yancin kananan hukumomi shi ne a kakkabe hannun gwamnoni gada harkokinsu. Gwamnoni suna yiwa hukumomin shiga sharo ba shanu lamarin da ya sa suka lalatasu.

Ga rahoto.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:08 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG