Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Manoma Da Makiyaya Da Masu Kiwon Kifi Sun Gudanar Da Babban Taro


Kungiyar manoma, makiyaya da masu kiwon kifi ta Afirka ta yamma ta gudanar da taro a birnin Abuja inda ta nuna cewa Afirka zata iya ciyar da kanta idan al’umma ta zage damtse.

Kungiyar ta dukkan manoma da lamuran karkara ta ce hana shigo da shinkafa Najeriya da shugaba Buhari yayi zai sa manoma da sauran al’umma azamar komawa gona.

Jibo Banye, daga jamhuriyar Nijer shine shugaban kungiyar yayi Karin bayanin cewa suna yabawa shugaba Muhammadu Buhari kuma suna goyon bayan sa dari bisa dari, domin a cewarsa bai kamata a ce shinkafa sai an shigo da ita daga wata kasa ba.

Taron ya sami halartar manoma da makiyaya, da wakilan manyan kabilu da wasu kananan kalbilun kasar, sun bayyana ra’ayoyin su akan yadda za’a magance arangamar da ake yawan samu tsakanin makiyaya da manoma a wasu yankunan kasar.

Wannan na faruwa ne daidai lokacin da ‘yan siyasa suka dawo da muhawara kan nada wasu da ba ‘yan siyasa ba a majalisar ministoci da shugaba Buhari yayi da suke gani haka na hana shi samun bayanai ko shawarwarin taimakawa al’ummar Najeriya da kuma talakawan yankunan karkara.

Ga cikakken rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya daga Abuja.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG