Kungiyar Taliban ta dauki alhakin harin da aka kaiwa sansanin sojojin Birtaniya a Afghanistan da ya yi sanadin kashe mayakan ruwan Amurka biyu.
Kakakin kungiyar ya bayyana yau asabar cewa, harin martani ne dangane da silman da aka hada a Amurka, da ya yiwa annabi Mohammadu batanci, kuma sabili da yariman Birtaniya Harry yana aiki a sansanin.
Kungiyar tsaro ta NATO tace mayakan sun kutsa cikin sansanin Baston dake lardin Helmand jiya asabar da dare suka kai hari a sansanin ta wajen amfani da kananan makamai, da roka da kuma ‘yan kunar bakin wake.
Kungiyar NATO tace, mayaka 18 suka mutu a harin yayinda aka jiwa daya rauni aka kuma kama shi. An jiwa dakarun kasa da kasa da dama rauni.
Jami’ai sun ce Yarima Harry wanda shine na uku a matsayin sarautar Birtaniya, bai shiga wani hadari ba. An tura shi aiki a sansanin ne a matsayin matukin jirgi mai saukar angulu. Kungiyar Taliban ta yi alwashin kashe shi.
Kakakin kungiyar ya bayyana yau asabar cewa, harin martani ne dangane da silman da aka hada a Amurka, da ya yiwa annabi Mohammadu batanci, kuma sabili da yariman Birtaniya Harry yana aiki a sansanin.
Kungiyar tsaro ta NATO tace mayakan sun kutsa cikin sansanin Baston dake lardin Helmand jiya asabar da dare suka kai hari a sansanin ta wajen amfani da kananan makamai, da roka da kuma ‘yan kunar bakin wake.
Kungiyar NATO tace, mayaka 18 suka mutu a harin yayinda aka jiwa daya rauni aka kuma kama shi. An jiwa dakarun kasa da kasa da dama rauni.
Jami’ai sun ce Yarima Harry wanda shine na uku a matsayin sarautar Birtaniya, bai shiga wani hadari ba. An tura shi aiki a sansanin ne a matsayin matukin jirgi mai saukar angulu. Kungiyar Taliban ta yi alwashin kashe shi.