Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kuskuren Asibitin Jami'ar Maiduguri Ya Nakasar da Wani Bawan Allah


Ciki da Gaskiya - Ibrahim Alfa Ahmed
Ciki da Gaskiya - Ibrahim Alfa Ahmed

Wani bawan Allah mai suna Ayuba Alamsin daga Chibok cikin jihar Borno ya bayyana yadda likitoci a Asibitin Koyaswa Na Jami'ar Maiduguri suka bashi maganin cutar da bashi da ita har gabobinsa suka mutu kana ya makance.

Shin wai idan likitoci a Najeriya suka yi kuskure babu wani hukumci da za'a yi masu ko kuma taimako da za'a iya yiwa wanda lamarin ya nutsa dashi?

Rayuwar Ayuba Alamsin ta gurbace kamar yadda zaku ji a wannan shirin na Ciki da Gaskiya na Ibrahim Alfa Ahmed.

Ayuba Alamsin har yanzu yana kai komo bai samu taimako ba kuma likitocin da suka tafka wannan ta'asa babu abun da doka ta yi masu.

Ga cikakken bayanin.

please wait

No media source currently available

0:00 0:10:20 0:00

XS
SM
MD
LG