Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ma'aikatan Ceto A Misra Sun Tsamo Gawarwakin Bakin Haure Daga Teku


Mutane na jiran gawarwakin da aka tsamo a teku
Mutane na jiran gawarwakin da aka tsamo a teku

Masu aikin ceto a Egypt a jiya Talata sun tsamo gawarwaki bakin haure da dama da suka nitse a cikin jirgin ruwar masunta a gabar tekun Mediterranean wanda ya kai a dadin wadanda suka mutu sama da dari biyu a hadarin jirgin ruwa da ya faru ran 21 ga watan nan na Satumba.

Wadanda suka tsira sun ce kamar mutane 450 zuwa dari shida cikin har da mata da kananan yara da dama aka cusa a cikin jirgin ruwar da ya nitse a garin Rosetta mai tashar jiragen ruwa, aka tasar wa nahiyar Turai.

Hukumomin sojin kasar Misra sunce galibin wadanda abin ya shafa duk ‘yan asalin kasar Masar ne daga yankin jihar Nile Delta kuma mafi yawansu matasa ne da suke kokarin ketarawa zuwa Turai don inganta rayuwarsu.

Amma kuma wasu rahotanni na cewar akwai ‘yan kasashen Afrika da dama da kuma wasu daga Syria a cikin jirgin.

Yan Sanda Masar sun fada a ranar Litinin an tsare mutumen da ya mallaki jirgin ruwan wanda zai iya huskantar shari’ar laifin yin simoga din mutane da da kuma kisan kai.

Hukumar yan gudun hijira ta duniya tace bakin haure dubu uku da dari biyar ne suka mutu ko kuma suka bata a wannan sheakara yayid da suke kokarin ketara teku Mediterranean.

Hukumar tace adadin ya nuna cewa mutanen da suka mutu a bana sunfi na bara da misalin mutane 600.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG