Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Murna Da Kubutar Da ‘Yan Matan Chibok


Majalisar Dinkin Duniya MDD ta ce tana marhaban da kubutar da yan mata 82 na makarantar Chibok da yan ta’addar Boko Haram suka yi garkuwa dasu a Najeriya, kuma ta yi kira ga iyalai da jama’a da a taimakawa wadannan yan mata da suke cikin dimuwa.

MDD ta ce tana kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su rike ‘yan matan da hannu biyu, kuma a basu taimako da suke bukata don su ci gaba da rayuwarsu tare da jama’a, inji kakakin sakataren MDD Antonio Guterres a jiya Litinin.

Kakakin Stephane Dujarric yace ana yin watsi da yan mata da aka taba yi musu fyade a cikin al’umma.

Sai dai shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi alkawarin sa ido da kansa a kan kyautata rayuwar ‘yan matan da aka kubutar dasu.

Gidauniyar kula da yawan al’umma ta MDD ta aika da rukunin masana a Najeriya ciki har da masu nasiha da likitoci da zasu taimakawa ‘yan matan su ci gaba da rayuwarsu.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG