Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Malaman Sabuwar Jami’ar Jihar Kano Sun Fara Yajin Aiki


Tattaunawar Shugaba Buhari da VOA Hausa Kan Ziyararsa A Amurka
Tattaunawar Shugaba Buhari da VOA Hausa Kan Ziyararsa A Amurka

Yau Kungiyar Malaman Sabuwar Jami’ar koyon aikin malanta ta Kano zata fara yajin aikin gargadi na mako guda,domin nuna bacin ransu game da matakin gwamnatin tarayya na soke Jami’ar tare da takwarrorinta dake Zaria da Owerri da kuma Ondo, da mayar dasu matsayinsu na baya wato kwalejojin ilimi.

Dangane da haka masana a fagen ilimi suka fara sharhi akan alfanu ko akasin sa dangane da wannan matakin na gwamnatin najeriya.

A hirarsu da wakilinmu Mahmud Ibrahim Kwari, Farfesa Salisu Shehu na Jami’ar Bayero Kano, kwararre kan nazarin aikin malanta ya bayyana cewa, daga matsayin wadannan kwalejojin ilimi alfano ne a fannin harkokin ilimi kasancewa kasar tana bukatar karuwar jami’oi, idan za a kwatanta da adadin jami’oin dake kasashen da basu kai Najeriya yawan al’umma da kuma karfin tattalin arziki ba. Ya bayyana takaicin ganin yadda ‘yan Najeriya ke zuwa karatu kasashen da basu kai Najeriya ba,

Farfesa Shehu ya kuma bayyana cewa, akwai bukatar kwararrun malamai. Yace babu jiha a arewacin Najeriya da zata buga kirji tace tana da kwararrun malamai a dukan kwasakwasai da maddodi na karatu da ake yi, wannan yana nuna, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tsaya tayi karatun ta-natsu, ta nazarci wadannan matsaloli kafin a yanke hukumci.

Farfesa Salisu Shehu yace idan akwai kurakurai a matakan da gwamnatin da ta gabata ta dauka a wannan fannin ana iya gyarawa a maimakon maida hannun agogo baya.

Ga cikakken rahoton da wakilin Sashen Hausa Mahmud Ibrahim Kwari ya aiko daga Kano, Najeriya.

Hira Da Farfesa Salihu Shehu-2:53
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG