Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan kasashen duniya sun bukaci tsagaia wuta a Siriya - John Kerry


John Kerry da wasu manyan kasashen duniya
John Kerry da wasu manyan kasashen duniya

Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya fada yau Jumma’a cewa, manyan kasashen duniya sun amince zasu bukaci a tsagaita wuta a yakin da ake yi a Syria, kuma ana sa ran matakin ya fara aiki nan da mako daya.

Jan Egeland, shugaban kwamitin Majalisar Dinkin Duniya a taron da ake yi kan batutuwan jinkai a Jamus, inda aka cimma wannan yarjejeniyar, yace “sai tayiwu wannan ne budin da ake dako.”

Miniustan harkokin wajen Turkiyya Mevlut Cavusoglu ya fada ta shafinsa a dandalin Twitter yau Jumma’a cewa, “wannan mataki yana da muhimmanci kan hanyar samo damar warware rikicin da ake yi a Syria.”

Sai dai anji Firayim Ministan Syria Dmitri Medvedev, yana gargadin manyan kasashen duniya cewa suyi tunani gameda tura sojojin-kasa zuwa Syria. A cikin sanarwa da ya bayar yau Jumma’a, yace, matakin sojin kasa zai iya tsunduma dukkan kasashe dake aiki kan rikicin cikin yaki.

Kerry ya gayawa manema labarai a birnin Munch cewa, shirin tsagaita wutar ba zai shafi kungiyoyin ‘yan ta’adda ba, da suka hada da ISIS, Al-Nusra d a dai sauransu.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG