Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan Malaman Islama Na Najeriya Sun Bayyana Goyon Baya Ga Yaki Da Polio


Ma'aikatan lafiya su na shirin digawa yara a Kano maganin rigakafin kamuwa da cutar shan inna, Polio
Ma'aikatan lafiya su na shirin digawa yara a Kano maganin rigakafin kamuwa da cutar shan inna, Polio

A bayan da suka halarci taron duniya kan yaki da cutar Polio a daular Abu Dhabi, malaman na Musulunci sun yi bitar mako guda ma 'yan'uwansu malamai a Abuja

Manyan malaman addinin Musulunci na Najeriya da suka halarci taron yaki da cutar Polio na duniya da aka yi a daular Abu Dhabi, sun gudanar da wata bitar mako guda a Abuja, babban birnin Najeriya, domin su fadakar da sauran 'yan'uwansu malamai irin muhimmancin dake tattare da tinkarar wannan cuta.

Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Hafizan al-Qur'ani ta Najeriya, Sheikh Musa Hassan, yana daya daga cikin wadanda a can baya suka yi adawa suka ki yarda da wannan allurar rigakafin, amma a yanzu yace ya gamsu dari bisa dari da wannan magani, kuma ya amince da cewa tilas ne a kawar da wannan cuta daga duniya baki daya, ba ma Najeriya kawai ba.

Shugabar Kungiyar Musulmi Mata ta Najeriya, maryam Idris Othman, ta ce yana da muhimmanci a wayar da kan mata domin shawo kan maza masu kin jinin wannan allurar rigakafin.

Ga cikakken rahoton da Nasiru Adamu el-Hikaya ya aiko daga Abuja kan wannan taron bita da irin bayanan da shaihunan malaman suka yi.

Manyan Malaman Islama Sun Tattauna Tare Da Bayyana Goyon Baya Ga Yunkurin Yaki Da Polio - 2:18
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:18 0:00
Shiga Kai Tsaye

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG