Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mataimakin kasar Masar ya ce Saukar Mubarak daga karagar mulki zai janyo rudami


Mai zanga zangar kin jinin gwamnati yana jifa da dutse a dandanlin 'yanci na birnin Alkahira
Mai zanga zangar kin jinin gwamnati yana jifa da dutse a dandanlin 'yanci na birnin Alkahira

Mataimakin Shugaban Kasar Misra, Omar Suleiman ya yi watsi da kiraye-kirayen Shugaba Hosni Mubarak ya yi murabus nan da nan

Mataimakin Shugaban Kasar Misra, Omar Suleiman ya yi watsi da kiraye-kirayen Shugaba Hosni Mubarak ya yi murabus nan da nan, ya ce wannan hanzarin zai haifar da rudami. Wannan jawabin nasa ya zo ne a daidai lokacin da masu zanga-zanga da jefe-jefen duwatsu su ka bijire wa dokar yana yawo a babban birnin kasar, al-Khahira, inda aka yi ta jin karar harbe-harben bindigogi a bisa tituna har zuwa dare. Masu zanga-zangar kin amincewa Mr Mubarak ya cigaba da zama bisa karagar mulki har sai karshen wa’adinsa, sun sha alwashin kaddamar da wata gagarumar zanga-zanga a gobe Jumma’a a yinkurinsu na matsa wa shugaban lamaba ya sauka. Saidai, Mr. Suleiman ya baiyana arangamar da aka yi tsakanin magoya baya da wadanda basu goyon bayan shugaba Mubarak a zaman makarkashiya. Yace babu hannun gwamnati amma za’a gano wadanda suka kitsa wannan makarkashiya.

XS
SM
MD
LG