Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matasa Sun Yi Watsi da Taron Kasa


Wasu cikin wakilan da zau halarci taron kasa
Wasu cikin wakilan da zau halarci taron kasa

Yayin da gwamnati ke shirin bude taron kasa matasan da Muryar Amurka ta zanta dasu babu dayansu da ya goyi bayan taron

Wakilin Muryar Amurka Ladan Ayawa ya samu ya zanta da matasa a birnin Legas dangane da taron kasa da za'a fara.

Wakilin Muryar Amurka Ladan Ayawa ya zanta da wasu matasa kan taron kasa da ma wakilan da zasu halarci taron. To saidai babu dayansu da ya amince da mahimmancin taron balantana ma wakilan da zasu halarci taron.

Dele Bamidele yace Najeriya ba kasar zama ba ce domin talauci ya yiwa kasar katutu. Yace talauci kadai ya zaunar da shi a kasar. Wannan taron baida kowane irin anfai balle ma wakilan dake wakiltarmu. Kasar da ba ruwa ba wuta ba wani abun more rayuwa, kai, komi game da Najeriya bai da kowane anfani balle wani taro ko kuma wakilan taron. Taron ba zai kawo karshen kowace matsala ba saidai ya bude masu wata hanyar kwasar kudi

Shi ma Akin Akala yace shi bashi da kwarin gwiwa a kan gwamnatin Najeriya. Su dai suna jiran sarautar Allah ce kawai. Yace taron kasa ko taron kwasar kudi!

Shi kuma Kunle Rashidi cewa yayi ana maganar yadda za'a yi karatu kai kana maganar taro. Wane taro? Muna gani karatu ya gagaremu. Jami'a ko ta gwamnatin tarayya ko ta jiha kowace tsada gareta alhali kuwa duk shugabanninmu babu wanda ya fuskanci rin wannan matsalar a nasu lokacin. Duk wadanda suka ga dama su sa a matsayin wakilanmu.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:08 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG