Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mayakan Ruwan Najeriya Na Nema A Yiwa Dokokin Kasar Gyaran Fuska.


Mayakan Ruwa suna hallartar taron sauyin shugabanci a birnin Abuja Junairu 20, 2014.
Mayakan Ruwa suna hallartar taron sauyin shugabanci a birnin Abuja Junairu 20, 2014.

Rundunar mayakan ruwan Najeriya ta bada shawarar yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska a fannin harkokin tsaro.

Babban hafsan mayakan ruwan Najeriya, Vice Admiral Ibok Ibas, yace rundunar zata ci gaba da kare diyaucin Najeriya.

Ya bayyana cewa, rundunar mayakan ruwan tana fuskantar kalubalai dake gurguntar da ayyukanta da suka hada da batutuwa irin na diplomasiya, yiwuwar rashin fahinta dake kasashen dake yankin tekun Guinea, da kuma farfaganda da Karin gishiri kan fashin teku da wadansu kafafen yada labarai na kasashen waje ke yi.

Vice Admiral Ibok Ibas ya kuma nemi da a yiwa dokokin kasar nan gyaran fuska, don baiwa sojojin damar, tuhuma da gurfanar da wandada ake zargi da aikata laifuka a cikin ruwa gaban kotu.

Bisa ga cewarshi, rundunar mayakan ruwan Najeriya tayi imanin cewa, idan aka sami kotuna na musamman dake sauraron irin wandannan shari’u, hakan zai karawa mayakan ruwan Najeriya kwarin guiwa.

Ga cikakken rahoton da wakilin Sashen Hausa Hassan Maina Kaina ya aiko daga Abuja, Najeriya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:14 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG