Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Miliyoyin Masu Cutar Kanjamau Ba Sa Samun Magani


Wata mai dauke da cutar kanjamau
Wata mai dauke da cutar kanjamau

Yayin da ake shirin kammala taron da ke dubi kan inda ake a yakin da ake yi cutar kanjamau ko kuma AIDS/SIDA a birnin Durban na Afrika ta Kudu a yau Juma’a, masana na shakkun ko za a iya shawo kan cutar nan da shekarar 2030.

Domin a cewarsu akwai miliyoyin mutane da ba sa samun maganin makarin wannan cuta wacce ta fi yawa a kasashen masu tasowa musamman a Nahiyar Afrika.

A cewar masanan, hukumomi ba sa maida cikakken hankali wajen yaki da cutar mai haddasa AIDS.

Sai dai kwararru a fannin kiwon lafiya sun ce sun dukufa wajen ganin an samu maganin cutar a duk fadin duniya.

Hajiya Maimuna Muhammed, tsohuwar mai shirya tsare-tsare ce a kungiyar NACA mai yaki da bazuwar cutar a Najeriya.

Jummai Ali ta tambaye ta shin za a yi nasarar kawar da wannan cuta kuwa?

Saurari wannan

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:38 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG