Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mun San Inda Daliban Chibok Suke - inji Sojojin Najeriya


Birgediya-janar Chris Olukolade
Birgediya-janar Chris Olukolade

​Wani babban jami'in sojin Nijeriya ya ce yanzu hukumar sojin kasar ta san inda masu kaifin kishin Islama su ke tsare da dalibai 'yan mata sama da 200 dinnan, to amma ya ce zai yi wuya a yi amfani da karfi wajen bukutar da su.

Babban Hafsa a Hedikwatar Tsaron Sojin Nijeriya Air Marshal Alex Badeh ya gaya ma manema labarai jiya Litini a Abuja cewa duk wani amfani da matakin soji zai zama da hadari ga 'yan matan. Ya ce, "Ba za mu kashe 'ya'yanmu da sunan yinkurin kwato su ba,"

Badeh, ya ce, "labari dai mai kyau ga iyayen 'yan matan shi ne mun san inda su ke, amma ba za mu iya gaya ma ku ba."

An sace 'yanmatan ne a tsakiyar watan Afrilu lokacin da su ke daukar jarabawa a wata makarantar sakandare da ke kyauyen Chibok da ke arewacin Nijeriya.

Mayakan sa kan kungiyar Boko Haram mai kaifin kishin Islama sun dau alhakin sace 'yan matan, kuma sun ce su na so a yi musayar 'yan matan da 'yan kungiyarsu da ke fursuna.

Kasashe da dama, ciki har da Amurka, na taimaka ma Nijeriya wajen neman 'yanmatan.
XS
SM
MD
LG