Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutane biyu sun hallaka a Najeriya sakamakon bindiga da wani bututun mai ya yi


Thick plumes of black smoke rise into the air after a petroleum pipeline explosion in Nigeria. (file photo)
Thick plumes of black smoke rise into the air after a petroleum pipeline explosion in Nigeria. (file photo)

Kafofin yada labarai a Najeriya da wasu shaidu sun bada labarin cewa wani bututun mai yayi mummunar bindiga ya kama da wuta har ya halaka mutane biyu

Kafofin yada labarai a Najeriya da wasu shaidu sun bada labarin cewa wani bututun mai yayi mummunar bindiga ya kama da wuta har ya halaka mutane biyu.‘Yansanda suka ce akwai alamun da gan-gan wani ya fasa bututun da yayi bindiga, ya kama da wuta yayin da wasu suke dibar mai a garin Amukpe dake kudancin jihar Delta. Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Charles Muka, yace bashi da bayanin yawan mutane da suka halaka, ya kuma ce hukumomi suna gudanar da bincike. Bututun mallakar kamfanin mai na Nijeriya watau NNPC ne.

XS
SM
MD
LG