Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutane Suna Kauracewa Jihohin Da Aka Kafa Dokar-Ta-Baci


Wata Mace da 'ya'ayanta da suke kokarin kauracewa Maiduguri
Wata Mace da 'ya'ayanta da suke kokarin kauracewa Maiduguri

Mazauna jihohin da aka kafa dokar-ta-baci suna kauracewa jihohin sakamakon rashin abinci da kuma zaman fargaba.

Jama’a da dama na ci gaba da kauracewa jihohin da aka kafa dokar-ta-baci zuwa wadansu jihohi da kuma kashe dake makwabta.

Rahotanni na nuni da cewa, mutanen da suke tafiya gudun hijira sun bayyana cewa, ya zama dole su kauracewa matsugunansu domin rashin kayan masarufi da muhimman ababan jin dadin rayuwa.

Sun kuma bayyana cewa, banda yunwa, suna zaune a cikin tashin hankali. Wadansu daga cikin ‘yan gudun hijiran da suka isa Gombe daga Maiduguri da wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya yi hira da su sun bayyana irin halin da suka shiga kafin suka isa garin Gombe.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:33 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG