Mun sami labarin mutuwar mutum na farko da ya soma saka kafarsa akan Wata, watau neil Armstrong.
Iyalin mamacin sunce a yau Assabar ne wannan dan sama-jannatin, 82, ya rasu a garin Cincinnati bayan wata rashin lafiyar da ta soma kama shi a farkon watan nan.
Neil Armstrong shine wanda yayi jagiorancin Kumbun Apollo 11 da ya sauka a kan Wata a ran 20 ga watan Yulin 1969. A wannan lokacin ne yayi wani kalamin da ya shiga tarihi inda, lokacinda ya dora kafarsa akan watan ya kada baki yace “wannan wani dan kankanen mataki a wurin mutum guda, amma gagarumin mataki ne a wurin halittar Bil Adaman duniya.”
Duniya ta tsaya cik tana kallon Armstrong yana wannan tattakin tareda dan’uwansa dan sama-jannati, Edwin “Buzz” Aldrin.
Iyalin mamacin sunce a yau Assabar ne wannan dan sama-jannatin, 82, ya rasu a garin Cincinnati bayan wata rashin lafiyar da ta soma kama shi a farkon watan nan.
Neil Armstrong shine wanda yayi jagiorancin Kumbun Apollo 11 da ya sauka a kan Wata a ran 20 ga watan Yulin 1969. A wannan lokacin ne yayi wani kalamin da ya shiga tarihi inda, lokacinda ya dora kafarsa akan watan ya kada baki yace “wannan wani dan kankanen mataki a wurin mutum guda, amma gagarumin mataki ne a wurin halittar Bil Adaman duniya.”
Duniya ta tsaya cik tana kallon Armstrong yana wannan tattakin tareda dan’uwansa dan sama-jannati, Edwin “Buzz” Aldrin.