A wata wasika da shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Bukola Saraki ya karanta a zauren majalisa, ya sanar da cewa mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, shine zai gudanar da lamuran ‘kasa a lokacin da Buhari ya tafi hutu.
Wata takarda da fadar shugaban ‘kasa ta aikewa manema labarai, na nuna cewa a lokacin wannan hutu da shugaba Buhari zai dauka, zai je ganin likita domin a duba lafiyarsa kamar yadda aka saba duk shekara.
Kundin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa shugaban kasa damar sanar da shugaban Majalisar Dattawa da na Wakilai kafin ya dauki hutu.