Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nelson Mandela Ya Kwanta A Asibiti


Tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Nelson Mandela kennan.
Tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Nelson Mandela kennan.

Tsohon shugaban Afirka ta Kudu Nelson Mandela ya koma asibiti domin neman maganin wani ciwo a hun-hunshi.

WASHINGTON, D.C - Wata sanarwa da ta fito daga ofishin shugaba Jacob Zuma tace a yammacin jiya laraba ne aka kwantar da Mr. Mandela, bayan da wani ciwo a cikin hun-hunshi ya kara tasowa, bayan da aka share makonni uku ana yi masa maganin irin wannan ciwo a watan Decembar da ta wuce. A wannan lokaci ne ma aka cire masa duwatsu daga cikin matsarmamar shi.

Mr. Zuma yau alhamis yayi wa dan shekaru tasa’in da hudu din, kuma mutumin da yaci lambar yabo ta nobel fatar samun lafiya, kuma ya nuna kwanciyar hankalinsa da likitocin da zasu duba Mr. Mandela.

Nelson Mandela dai ya shere sama da shekaru 30 a gida yari, saboda adawa da yayi da turawan mulkin mallaka da wariyar launin fata, kuma ya zama jigo wajen samar da mulkin demokradiyya ta hanyar lumana a wannan kasa. Shine ya zama bakar fata na farko da ya shugabanci Afirka ta Kudu.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG