Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar: A karon farko 'yan siyasa masu tarin yawa zasu tsaya takara


Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou kuma daya daga cikin 'yan takara 16
Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou kuma daya daga cikin 'yan takara 16

Kawo yanzu 'yan takara goma sha shida ne suka fito tsayawa takarar neman shugabancin kasar ta Nijar

Za'a yi zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki ranar 21 ga watan Fabrairu mai zuwa.

Masu kula da alamuran dake faruwa na ganin fitowar 'yan takara masu tarin yawa wata alama ce na cigaban dimokradiya da kasar ta samu tunda aka fara mulkin farar hula kimanin shekaru 21 da suka wuce.

Wani Dambaji dan gwagwarmaya a karkashin wata kungiya yace idanun 'yan Nijar sun bude akan harkokin siyasa. Yace ko mutanen daji sun fahimta, sun gane menene dimokradiya.

Shigar matasa cikin siyasar kasar ta sa mutane na tofa albarkacin bakinsu. Masaud Ibrahim yace sakamako ne na rarrabuwar kawunan wasu manyan jam'iyyun siyasa da suka fuskanta cikin shekarun baya bayan nan.

Rashin samun mace ko daya cikin 'yan takara goma sha shida nada nasaba da rashin kudi da mata ke fama dashi. Matsalar Boko Haram ta hana mata shiga daji nman kuri'u.

Kotu zata tantance 'yan takaran ranar tara ga wannan watan.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:34 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG