Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Pakistan Ta Koka Ga Hukumomin NATO


مصر کے برطرف کے گئے صدر محمد مرسی کے حامی فوج کے انتباہ کے باوجود دارالحکومت قاہرہ میں بدستور دھرنے دیئے ہوئے ہیں۔
مصر کے برطرف کے گئے صدر محمد مرسی کے حامی فوج کے انتباہ کے باوجود دارالحکومت قاہرہ میں بدستور دھرنے دیئے ہوئے ہیں۔

Wannan ya biyo bayan gwabzawa tsakanin sojojin Pakistan da jiragen yakin NATO a bakin iyakar Pakistan da Afghanistan

Rundunar sojojin Pakistan ta mika takardar kuka da babbar murya, a bayan da aka yi musayar wuta a tsakanin sojojinta da jiragen helkwafta na NATO a bakin iyakar Pakistan da Afghanistan.

Pakistan ta ce sojojinta dake wata tashar bakin iyaka sun bude wuta talata da safiya a lokacin da wadannan jiragen saman helkwafta suka kutsa cikin yankin Pakistan. Ta ce sojoji biyu sun ji rauni a musayar wutar da aka yi.

NATO ta tabbatar da cewa akwai wasu helkwaftocinta da suka yi shawagi a yankin bakin iyakar, ta kuma ce tana binciken al’amarin.

Wani jami’in soja na wata kasar yammaci a Kabul yace helkwaftocin su na bangaren Afghanistan na bakin iyaka a lokacin da aka bude musu wuta daga cikin Pakistan. Yace daya daga cikin helkwaftocin ya maida martani, a bayan da aka yi harbi kansa har sau biyu.

Wannan musayar wuta ta jiya talata a kusa da yankin Datta Khel a lardin Waziristan ta Arewa, ta zo a daidai lokacin ad tankiya ta karu a tsakanin Amurka da Pakistan, a bayan farmakin da Amurka ta kai ta kashe shugaban al-Qa’ida, Osama bin Laden, a birnin Abbottabad.

XS
SM
MD
LG