Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ra’yoyin Wasu ‘Yan Jihar Borno Game Da Sakin ‘Yan Matan Chibok 82


Shugaba Muhammadu Buhari Da 'Yan Mata 82 Da 'Yan Boko Haram Suka Sako
Shugaba Muhammadu Buhari Da 'Yan Mata 82 Da 'Yan Boko Haram Suka Sako

Biyo bayan nasarar da gwamnati Najeriya ta samu na cimma yarjejeniya da kungiyar Boko Haram, inda aka sako wasu daga cikin ‘yan matan Chibok har su 82 shugabannin da mutanen jihar Borno sun tofa albarkacin bakinsu.

Gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima, ya yi bayani ga al’ummar jiharsa da kuma mika godiyarsa ga shugaba Mohammadu Buhari da kuma rundunar sojan kasar game da nasarar da suka samu na sake ‘yanto ‘yan matan Chibok.

Da suke bayyana ra’yoyinsu wasu mazauna garin Maiduguri, kan sakin ‘yan matan Chibok da aka yi shine rashin samun cikakken bayani game da ‘yan kungiyar Boko Haram din da aka yi musayarsu da ‘yan matan 82.

Abin tambaya dai anan shine manene makomar mayakan Boko Haram din da aka saka? Shin zasu koma su dauki kayan yaki su ci gaba da kashe al’umma ko kum sun tuba? Yanzu dai abin da al’umma ke jira su gani shine cikakken bayanan irin yadda aka kubutar da ‘yan mata da kuma irin halin da suke ciki.

Domin karin bayani saurari rahotan Haruna Dauda Biu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG