Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikici a Jam'iyyar APC ta Najeriya


Alhaji Nuhu Ribadu
Alhaji Nuhu Ribadu

Tsohon Dan takarar jam’iyyar APC Nuhu Ribadu, yayi zargin cewa PDP ce ke haddasa cece-kuce a cikin jam’iyyar.

A daidai lokacin da rikicin cikin gida ke kara Ta’azzara a rassan jam’iyyar Hamayya ta APC, tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar ACN, Malam Nuhu Ribadu yayi zargin cewa akwai hannun jam’iyyar PDP wajen shirya fitina a jam’iyyar ta PDP.

Hakan na faruwa ne a daidai lokacin da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC da suka hada da tsohon Gwamnan mulkin soja a jihohin Borno da Lagos, Janar Buba Marwa da wasu gaggan jam’iyyar APC ke kauracewa taron shugabannin jam’iyyar APC a jihar.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:33 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG