Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rundunar sojan Nigeriai ta gano makarkashiyar Boko Haram


Sojojin Nigeria
Sojojin Nigeria

Rundunar sojan Nigeria a Maiduguri, arewa maso gabashin Nigeria tace, ta gano wata makarkashiya da yan Boko Haram su ke shirin kitsawa na kai hare hare

Rundunar sojan Nigeria dake birnin Maiduguri jihar Borno arewa maso gabashin Nigeria tace, ta gano wani shiri da yan Boko Haram ke yi na amfani da unifam din masi aikin agaji domin kai hare hare a wuraren ibada.

Kwamandan rundunar soja shiya na bakwai, wanda kuma yake kula da jihohi shidda na arewa maso gabashin Nigeria Janaral Yusha'u Abubakar shi ya yiwa manema labaru bayanin makarkashiyar da suka gano a Maiduguri.

Haka kuma Janaral Abubakar yace sun kama daya daga cikin mutane dari 'yan Boko Haram da suka gabatar da hotunan su. Wanda aka kaman sunansa Danldi Abdullahi, kuma shine lamba na 26 cikin jerin sunayen yan Boko Haram da rundunar sojan Nigeria ta gabatar da sunayensu da kuma hotunan su.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:28 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG