Takaddamar da ta kunno kai a yanzu tsakanin tsofaffin ‘yan majalisar da sababbi, a game da manyan mukamai kamar na kakakin majilisar wakilai da kuma na shugaban majalisar dattawa, sababbin ‘yan majalisar dake da rinjaye a majalisar dokokin na ganin an canja tsarin mulkin majalisar da aka dade ana amfani da shi, wanda ya samo asali tun da aka fara mulkin farar hula a Najeriya.
‘yar majalisar wakilai kuma wadda ta sake samun nasarar lashe zabe a bana Khadija Bukar Abba Ibrahim, tace, “akwai dokoki da suka ce sababbi ‘yan majalisa na dokoki dana wakilai ba zasu iya takarar wasu mukamai ba,” wanan wani tsarin kuduri ne na majalisar wanda ya dade ana aiki da shi a kasar.
Kodayake a cikin ‘yan jam’iyyar APC masu rinjaye akwai masu goyon bayan sabbin da suyi hakuri, su baiwa wanda suka kware dama. Injiniya Yunusa Ahmed Abubakar, sabon ‘dan majalisar wakilai ne daga jihar Gombe kuma yana daga cikin masu wannan tunanin, inda yace, “Mu muyi hakuri sabbi da muka shigo, idan bamu baiwa masu kware wa a kai yi ba to gaba in muka dawo zamu ga muhimmancin kwarewar.”
Aikin majalisa dai ba’a koyar dashi a wata makaranta ko jami’a, dole ne abakin aiki ake koyarsa har a kware.