Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sabon Hafsan Sojin Somaliya Ya Tsallake Rijiya Da Baya


Sabon Hafsan sojin Somaliya, Janar Ahmed Muhammed Jimale Irfid, ya tsallake rijiya da baya a wani harin kunar bakin waken da ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 15 kusa da tawagarsa a Mogadishu, a cewar jami'an gwamnati.

Fashewar ta auku ne bayan da sabon Ministan Tsaro Abdurrashid Abdullahi Mohammed da kuma tsohon Hafsan soji Janar Mohammed Aden su ka bi ta hanyar, a cewar majiyoyin tsaro.

Sabon Hafan sojin na Somaliya na dawowa ne daga wata hidima a Ma'aikatar Tsaron kasar, inda ya maye gurbin Janar Aden.

An ce akasarin wadanda fashewar ta rutsa da su fararen hula ne da ke cikin wasu motocin bus-bus biyu.

Kungiyar mayaka ta al-Shabab ta yi ikirarin kai harin.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG