Ranar Talatar da ta gabata ne dai ministan Shari’a na Najeriya Abubakar Malami, ya kaddamar da kwamitin a madadin shugaba Mohammadu Buhari.
Kwamitin wanda ke karkashin jagorancin tsohon shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Ken Nnamani. An daura masa alhakin tuntubar masu ruwa da tsaki kan yadda za a inganta lamuran zabe a Najeriya. Haka kuma kwamitin na da hurumin nazari akan rahoto da kuma shawarwarin kwamitin gyaran zabe da marigayi shugaba Umaru Musa ‘yar Aduwa ya kafa, karkashin jagorancin tsohon babban Jojin tarayya Mohammad Lawal.
Tuni dai kungiyoyin rajin dimokaradiya sukace sun daura damarar sanya idanu sosai, domin ganin gwamnati ta aiwatar da rahotan kwamitin kamar yadda ya kamata.
Saurari cikakken rahotan Mahmud Ibrahim Kwari daga Kano.