Ziyarar da Mr Kerry ya kai Asiya ta tsakiya,tazo ne bayan rangadi da ya kai Turai da kuma Gabas ta Tsakiya. A jiya Lahadin ya gana da shugabannin kasashe biyar wadanda da suke karkashin ikon kasar Rasha da can wato, Kazakhstan,Kyrgyzstan,Tajikistan, Turkmenistan da kuma Usbekistan, kasashen da duka suke nuna damuwa kan sake farfadowar kungiyar Taliban a Afghanistan da kuma shigar 'ya'yan kasashen cikin kungiyar ISIS. Babban jami'in difilomasiyya na Amurkan yayi magana kan wadannan batutuwa a ganawar da suka yi a birnin Samarkand.
Jami'an Amurka suna kallon ziyarar da Mr. kerry ya kai a zaman matakin kara tabbatarwa kasashen da suke yankin Asiya karfin danganatakarsu da Washington, a dai dai lokacinda dangantaka tsakanin Amurka da Rasha take tabarbarewa. Haka nan ma akwai matsin lamba kan Mr.Kerry yayi magana kan rashin mutunta hakkin Bil'Adama da shugabannin suke aikatawa.