Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sake Tsugunnar Da Al’umomin Da Rikicin Boko Haram Ya Shafa


International Rescue Commitee IRC
International Rescue Commitee IRC

Kungiyar bada tallafi ta kasa da kasa ta International Rescue Committee da ake kira IRC a takaice, ta ce zata cigaba da tallafawa na Najeriya wajen sake tsugunar da al'umomin da rikicin Boko Haram ya shafa.

Ita dai wannna kungiyar na cikin kungiyoyin dake bada tallafi ga al'ummomin da bala'o'i da kuma tashe tashen hankula ke shafa a duniya.

Yayin wata ziyarar data kai jihar Adamawa, jami'ar kungiyar a Najeriya, Malama Sarah Ndikumana, ta ce dole a hada hannu wajen agazawa al'ummomin da rikicin Boko Haram ya shafa a Najeriya. kuma baya ga jihar Adamawa kungiyar na bada irin wannan tallafi a jihohin Borno da Yobe, da suma ke fama da matsalar Boko Haram.

Tun farko da yake wa tawagar ta IRC maraba, gwamnan jihar Adamawa Bindo Jibrilla, ya yaba ne da irin taimakon da irin wadannan kungiyoyi ke badawa ga mutanen da rikicin Boko Haram ya shafa.

Kuma wannan ma na zuwa ne yayin da kasar Kamaru ke haramar sake iza keyar yan Najeriya fiye da dubu 56 da yanzu haka ke gudun hijira a Kamaru.

Domin karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:04 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG