Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Saurari Jawabin Janar Buhari a kasa


Jam’iyyar CPC tana kira ga magoya bayanta kada su yar da da abinda ta kira wasu bata gari suna fakewa dasu suna barnar rayuka da dukiyoyin jama’a,da sunan bayyana rashin amincewar su da sakamakon zaben shugaban kasa da aka bayyana.

Dan takarar shugaban kasa,kuma tsohon shugaban kasa a zamanin mulkin soja Janar Muhammadu Buhari ne, ya yi wan nan kira lokacin da yake magana da manema labarai kan tarozmar da ta biyo bayan bayyana sakamakon zaben shugaban Najeriya.

Janar Buhari yace “ ta’asar kona wuraren ibadu da wasu laifuffuka da aka aikata” sun dara ma satar kuri’a da aka yi.

Dan takarar shugaban kasan ya bayyana godiya magoya bayan jam’iyyar, ya kuma nemi su kara hakuri,jam’iyyar zata dauki matakan kwato musu hakkinsu.

Saurari hirar janar Buhari a kasa

Saurari Jawabin Janar Buhari a kasa

Hirar Janar Buhari

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG