Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shaikh Dahiru Bauchi Ya Kira Buhari Ya Sake Salo Ya Rage Kuncin Rayuwa


Shaikh Dahiru Usman Bauchi
Shaikh Dahiru Usman Bauchi

Matsalar tsadar rayuwa a Najeriya ke ci ma talakawa tuwo a kwarya saboda haka ne shugabanni na addini da na al'umma ke kiran gwamnatin kasar da ta sauya salo ko talaka zai samu dan sassauci.

Bayan sun kammala taronsu na darikar Tijjaniya da suka gudanar a Yola babban birnin jihar Adamawa, Shaikh Dahiru Bauchi, daya daga cikin shugabannin addinin musulunci a Najeriya yana ganin dole ne gwamnatin tarayya ta tashi tsaye ta magance matsalar kuncin rayuwa da ake fama da ita a kasar yanzu.

Shaikh Dahiru Bauchi yace a ji tausayin mutane saboda suna cikin wahala musamman wahalar abinci. Yace a tausaya masu a samu hanyar da za'a tare abincin da aka noma cikin gida domin kada a yi waje dashi. Wanda ma yake waje a shigo dashi a kara kan na gida.

Malamin ya ci gaba da cewa a dubi duk abubuwan da suka dami mutane a yi masu maganinsu kama daga gwamnatin tarayya zuwa na jihohi da na kananan hukumomi. A tausayawa jama'a.

Yayinda ya juwa kan takunsakan da ake samu da 'yan kungiyar Shi'a da hukumomin kasar, Shaikh Bauchi yace akwai abun dubawa. A hada kai tsakanin musulmai da makwaftansu da ba musulmai ba domin a zauna lafiya. Kowa yayi abun dake gabansa tunda kasar ta ba kowa damar yayi addinin da yake so. Yace to kowa yayi nasa kada a tsangwameshi, shi kuma kada ya tsangwami kowa.

Yace kodayake tashin hankali a arewa maso gabas yayi sauki amma ta wajen Zamfara sai karuwa yake yi. Suna rokon Allah ya kawo sauki.

Ga rahoton Ibrahim Abdulaziz da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:12 0:00

XS
SM
MD
LG