Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sheik Dahiru Bauci Yace Musulmai Basu Yarda Gwamnati Ta Tsame Hannun Ta ba Daga Gudanar Da Ayyukan Hajji


Nigeria Muslims offer prayers during Eid al-Adha prayers to mark the end of the holy month of Hajji.
Nigeria Muslims offer prayers during Eid al-Adha prayers to mark the end of the holy month of Hajji.

A taron manema labarai da Musulman suka kira a , Mallam Dahiru Bauci ya tattauna da wakilin sashen Hausa Abduwahab Muhammed kan wannan batu.

Inda ya fara da cewa akwai maganganun da suka soma yawo cewa gwamnati ta fidda hannun ta ciki harkan alhazai.

Yace su mutanen Najeriya musulmai basu goyi bayan hakan ba.

Yace dan Najeriya duk inda yake a duniya akwai hannun gwamnati akansa ba za’ace idan ya fita Najeriya ba ruwan sa da gwamnati ba ko kuma ba ruwan gwamnati dashi ba zai yiyu ba.

Kuma ‘yan Najeriya yawanci suna rashin bin doka, wannan ma yana faruwa da hannun gwamnati balle ace yau ba hannun gwamnati, wannan zaisa a rika yiwa mutane yadda aka ga dama.

Sheik Dahiru Bauci yacemusali kudin da za’a biya na tafiya aikin hajjin ba za’ayi musu iyaka ba, abubuwan da za’ayi musu babu iyaka.

Babban malamin yace abin zai koma ba tsari Kenan

Ga Abdulwahab Mohammed da ci gaban hirar tasu

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00

XS
SM
MD
LG