Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ZABEN2015: Shin Farfesa Jega Waliyyi Ne?


Farfesa Jega
Farfesa Jega

Farfesa Attahiru Jega ya sha zagi a zaben shekarar 2011 a zaben da ya ba Jonathan damar darewa karagar mulki, sai kuma ga zaben 2015 ya ba Buhari damar lashe mafi yawancin kuri'un 'yan Najeriya. Wadanda suka yi tir da Jega sai ga shi a yanzu suna masa kallo wani waliyyin da ya zame musu maceci.

A zaben shekarar 2011 da ya kai ga SHugab Jonathan darewa karagar mulkin Najeriya a matsayin zababben shugaba ya jawo kace nace har ma da zubar da jini sakamakon zaben da ya tandara Buhari da kasa.

Shi kuwa shugaban hukumar zaben Farfesa Attahiru Jega ya sa zagi da wake-waken batanci daga ‘yan Najeriya tare da zargin an saye shi ne shi yasa yace Jonathan ne ya ci zaben.

A wannan shekarar kuma ta 2015 ne aka gudanar da wani zaben da ya kai Muhammad Buhari ga zama sabon zababben Shugaban mai jiran gado, sannan kowa sai murna da farin ciki musamman ma dai ‘yan Arewa da a da suna ganin an mummurdewa Buhari zabe.

Nasiru Adamu El-Hikaya ya sami Jega inda yayi hira da shi game da jin makomar masu zagin a wajensa, wadanda suka dawo kuma suna yabon Farfesan a yanzu.

“Mun ji dadi an yi zaben nan kuma kowa ya yawa har da masu sa idon kasashen waje duk sun yaba. Sannan na’urar da muka shigo da ita ta yi aiki bisa yadda muka bukata".

Duk abinda muka yi a baya adalci muka yi kokarin yi. Jegan ya bayyana cewa shi adalci ana wa kowa kamar yadda addini ya nuna. Ya kuma nuna ya yafewa duk masu zaginsa da kuma neman Allah yasa mu tsayawa adalci tare da godiya ga Allah.

Amma yanzu a shekarar 2014 data gabata kudin da muka samu sun koma dala biliyan 77. Hakan yana da alaka da maganar siyasa.” Kamar yadda Bintube ya bayyana. Ya kara da cewa maganar barazanar cewa ‘yan kudu zasu yi bore in basu ci zabe bay a taimaka wajen kawo nakasu inda masu zuba jari suka dinka kwashe nasu ya nasu suna barin Najeriyar.

Abin jira anan shine, yadda makomar darajar Naira idan zababben shugaban kasar Muhammadu Buharti ya karbi ragamar mulki daga hannun shugaba Jonathan Goodluck zata kasance.

Shin Farfesa Jega Waliyyi Ne - 2'55"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:55 0:00

XS
SM
MD
LG