Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Salva Kiir Yayi Barazanar Jagorancin Afkawa Kungiyoyin Tsageru


Shugaban kasar Sudan ta Kudu, Silva Kiir, yayi barazanar cewa shi da kansa zaiyi jagorancin mayakansa suje su abkawa kungiyoyin tsageru dake tsakiyar kasar idan basu daina kai hare-hare akan fararen hular kasar ba.

A jiya ne shugaban yake cewa zai shiga gaba, soja su bi baya don suje Kogin Yei, su ja daga da wadanan ‘yan tsageran dake yawan kai hare-haren akan fararen hulan dake shigewa ta kan titunan dake kusa da kogin.

Ko a cikin makon jiya su ma jami’an MDD sun la’anci wadanan hare-haren da ake kaiwa a wannan yankin, wadanda ake jin watakila suna da alaka da kabilanci a tsakanin al’umman wurin.

XS
SM
MD
LG