Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Angola zai bar faggen siyasa bayan wa'adinsa a shekarar 2018


Shugaban Angola Jose Eduardo dos Santos.
Shugaban Angola Jose Eduardo dos Santos.

A yau Juma’a shugaban kasar Anogla, Hose Eduardo dos Santos, wanda ya kasance daya daga cikin shugabannin Afrika da suka dade akan karagar mulki, ya ce zai yi ritaya daga harkokin siyasa idan wa’adinsa ya kare a shekarar 2018.

A lokacin da ya ke ganawa da shugabannin jam’iyar MPLA a Luanda babban birnin Angola, Santos ya ce zai ajiye harkar siyasa baki daya.

A watan Satumbar shekarar 2017 wa’adin Santos zai kare, sai dai shugaban bai ambaci dalilin da ya sa zai sauka daga mulki a shekarar ta 2018 ba, sannan bai fadi maksudin shirin na sa na yin ritaya ba.

Dan shekaru 73, Dos Santos ya kasance a akan karagar mulki tun daga shekarar 1979.

Shi ne na biyu a jerin shugabannin Afrika da suka fi dadewa akan mulki, bayan Teodoro Obiang Nguema na kasar Equatorial Guine.

Masu sukan shugabancinsa, suna zarginsa da yin amfani da mukaminsa wajen azurta kansa da abokanansa da kuma iyalansa ta hanyar wawure kudin man kasar.

XS
SM
MD
LG