Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin Kasashen Afirka Ta Yamma Suyi Takatsantsan Kan Gambia - Janar Abubakar


Sugabannin kasashen Afirka ta Yamma da aka dorawa alhakin sasanta rikicin siyasar kasar Gambia. Daga hagu Shugabar Liberia Ellen Sirleaf, da shugaban Najeriya Buhari da na Senegal Sall
Sugabannin kasashen Afirka ta Yamma da aka dorawa alhakin sasanta rikicin siyasar kasar Gambia. Daga hagu Shugabar Liberia Ellen Sirleaf, da shugaban Najeriya Buhari da na Senegal Sall

Tsohon shugaban Najeriya Janar Abdulsalami Abubakar ya kira shugabannin kasashen Afirka ta Yamma dake kokarin shiga batun kasar Gambia dake neman fadawa cikin rudanin siyasa, da suyi takatsantsan

Janar Abdulsalami Abubakar wanda ya kware a sasanta rikicin siyasa a kasashen Afirka ya yi magana ne a wurin jana'izar tsohon gwamnan jihar Neja Injiniya Abdulkadir Kure.

Inji Janar Abubakar lamarin kasar Gambia nada matukar tayar da hankali. Shawarsa ita ce yadda za'a lallaba Yahya Jammeh ya yadda an kadashi a zaben da ya gabata. Kuma tunda yake yayi mulki har na shekaru 22 yayi hakuri ya sauka domin ba gado ba ne. Ya ba kasarsa lafiya da zama lafiya inji Janar Abubakar.

Yace yadda aka yi zabe da can yaci haka ma aka yi zabe a wannan karon shi Adamu Barrow yaci, saboda haka yayi hakuri ya mika mulki. Ya kira shugabannin kasashen yammacin Afirka da su bi Yahya Jammeh da hankali, bada mugun kalami ba ko wata barazana ba.

Ga rahoton Mustapha Nasiru Batsari da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:56 0:00

XS
SM
MD
LG