Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojoji Sun Fatattaki 'Yan Boko Haram Daga Damaturu


Sojoji
Sojoji

Jami’an tsaro, a Damaturu babban birnin jihar Yobe sun fatattaki, ‘yan bindiga, da ake zato 'yan kungiyar Boko Haram ne, da suka yiwa garin Damaturu.

Jami’an tsaro, a Damaturu babban birnin jihar Yobe sun fatattaki, ‘yan bindiga, da ake zato 'yan kungiyar Boko Haram ne, da suka yiwa garin Damaturu, diran, mikiya da sanyin safiyar yau litinin.

Rahotanin na nuni da cewar an farma ‘yan bindigan ne, ta sama da kasa inda Sojoji suka fatattake ‘yan bindigar da ake zaton cewa ‘yan Boko Haram ne.

Da sanyin safiyar yau ne suka farma Jami’ar, jihar Yobe, rahotanin sun na nuni da cewa ‘yan kungiyar ta Boko Haram sun shigo garin Damaturu, ne ta kudu ta hanyar Gujjuba.

Koda yake jama'ar garin Damaturu a wannan karo sun yabawa jami'an tsaro saboda sunyi rawar gani wajen fatattakar 'yan kungiyar Boko Haram, daga Damaturu.

Sojoji Sun Fatattaki 'Yan Boko Haram Daga Damaturu - 2'10"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:10 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG