Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Najeriya Zasu Ga Bayan Boko Haram


Sojojin Najeriya
Sojojin Najeriya

A firar da yayi da Muryar Amurka mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriya Kanal S.K.Usman ya tabbar da niyarsu akan kungiyar Boko Haram na kawo karshen 'yan ta'adan gaba daya

Kwana kwanan nan 'yan kungiyar Boko Haram suka sake fitar da wani faifan bidiyo suna ikirarin galabar da suke samu akan sojojin Najeriya.

Kanal S. K. Usman yace bidiyon wani abu ne na neman tasiri amma bashi da wani tushe balle makama. Ikirarin da suke yi ba gaskiya ciki. An rurushe wurarensu da dama kuma an tarwatsasu. Kawo yanzu babu inda suka kama. Yace "mun lashi takobi sai mun ga bayan kungiyar Boko Haram da ta'adanci a wannan kasa tamu"

Bidiyon baya bayan nan bai nuna shugaban na kungiyar ba Abubakar Shekau abun da shi S.K. Usman yace wannan bai damesu ba. Ko da shugaban ko babu shi abun da suka sa gaba shi ne ganin bayan kungiyar da ta'adanci.

Yace da suna da kamarin da zasu kai farmaki amma yanzu babu shi. Yanzu su ne ak nema. Abun da suke so yanzu shi ne duk wani ta'adanci an ga bayanshi.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:13 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG