Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Takaitatcen Tarihin Sakatariyar Gwamnatin Najeriya Dr. Habiba Lawal


Dr. Habiba Lawal sakataren gwamnatin tarayya mai riko
Dr. Habiba Lawal sakataren gwamnatin tarayya mai riko

Ta karantu ta kuma yi aikace aikace a fannoni daban daban a mataki jihar da na tarayya

Mai rikon mukamin sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya, Dr. Habiba Lawal, ‘yar asalin karamar hukumar Toro ne dake jihar Bauchi,

An haifeta a ranar 3, ga watan yuni shekarar 1963, tayi karatun firamare a makarantar firamare na Gyamzo a garin Toro, daga nan sai karatun sakandare wanda tayi a kwalejin gwamnatin tarayya dake Kaduna.

Bayan da ta kammala karatun sakadare sai ta nufi jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria, a inda tayi digiri dinta na farko da na biyu, daga bisani kuma ta tafi jami’ar Abubakar Tafawa Balewa inda tayi digirin digirgir.

Har ila yau tayi wani karatun a wata jami’a mai suna Anglia a kasar Biritaniya.

Dr. Habiba Lawal, ta yi koyarwa a jami’ar Abubakar Tafawa Balewa, dake Bauchi, tayi kwamishina, a ma’aikatun ciniki da masana’antu da ma’aikatar al’adu da yawon bude ido a jihar Bauchi, ta kuma rike mukamai daban daban a matakin gwamnatin tarayya.

Dr. Habiba Lawal, ita ke rike da mukamin babbar jami’a a ofishin sakataren gwamnatin tarayya kawo lokacin da aka tabbatar mata da mukamin sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya amma a matsayi na riko.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:16 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG