Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Kasa Na Iya Kara Rarraba Kawuna: Sen Maccido


Bukukuwan Ranar Samun 'Yancin Najeriya.
Bukukuwan Ranar Samun 'Yancin Najeriya.

Shugaban kwamitin kasafin kudi a majalisar dattijan Najeriya Ahmed Muhammad Maccido ya bayyana cewa, bai ga amfanin taron tuntuba na kasa da ake shirin yi a Najeriya ba.

Shugaban kwamitin kasafin kudi a majalisar dattijan Najeriya Ahmed Muhammad Maccido ya bayyana cewa, bai ga amfanin taron tuntuba na kasa da ake shirin yi a Najeriya ba.

Saneta Maccido yace idan ba a yi hankali ba taron yana iya kara rarrabuwar kawuna a maimakon cimma manufar da ake tsammani. Bisa ga cewarshi, wadansu suna iya zuwa su kasa kai zuciya nisa a maimakon gyara su rika zagin juna.

A cikin hirarsu da Sashen Hausa yayin wata ziyara da ya kawo tashar, Saneta Maccido yace kowanne bangare zai dandana kudarshi idan Najeriya ta rarrabu kamar yadda wadansu suke neman ganin an yi.

Da yake magana dangane da dambarwar siyasar jam’iyarsu ta PDP, dan majalisar ya bayyana cewa, abinda ya kawo sabani tsakanin ‘yan jam’iyar shine rashin tattaunaw da kimanta gaskiya da adalci. Ya kuma ce batun cire shugaban jam’iyar Bamanga Tukur da kuma batun tsayawa takarar shugaba Goodluck Jonathan batutuwa ne da suke takarda kawai amma akwai batututwa da dama da ‘ya’yan jam’iyar da suka balle suke neman ganin an yi kafin a koma inuwa daya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:49 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG