Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Kolin China Da Kasashen Afirka


Gwamnatin kasar China na tayi tayin dalar Amurka Miliyan dubu 60 bashi da kuma taimako don zaburar da cigaban Afirka, wannan shine alamar yadda kasar ke kara kusanci ga nahiyar Afirka.

Gwamnatin kasar China na tayi tayin dalar Amurka Miliyan dubu 60 bashi da kuma taimako don zaburar da ci gaban Afirka, wannan shine alamar yadda kasar ke kara kusanci ga nahiyar Afirka.

Shugaban kasar China Xi Jinping, ya fitar da sanarwar ne a yau Juma’a a wani taron kolin China da kasashen Afirka da akeyi a birnin Johannesburg.

Shugaban dai yayi alkawarin ba zai sa kai ba ga lammuran siyasa a nahiyar ba, inda yake cewa, “China tayi imanin cewa nahiyar Afirka ta mutanen Afirka ce, kuma matsalar Afirka kamata yayi mutanen Afirka su warware kayar su.”

Gwamantocin yammacin duniya na ganin laifin China, na rashin kulawa kan yaki da kare ‘yan cin bil Adama a Afirka, a lokacin da Chinar ke ci gaba da harkokin kasuwancinta a nihiyar.

Shugaban kungiyar tarayyar Afirka kuma shugaban kasar Zimbabwe Robert Mogabe, yace yana yin abinda ya ke tsammanin kasashen da sukayi mulkin mallaka za su yi.

XS
SM
MD
LG