Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tashin Bom a Jos Nigeria ya Kashe Mutane Biyu


In this image taken from TV showing the bodies of victims of inter-faith violence as a crowd gathers around, in the town of Dogo Nahawa, Nigeria, south of the city of Jos (File Photo)
In this image taken from TV showing the bodies of victims of inter-faith violence as a crowd gathers around, in the town of Dogo Nahawa, Nigeria, south of the city of Jos (File Photo)

‘Yan sanda a birnin Jos, jihar Plateau Nigeria, sun bada rahoton kara samun fashewar bom a Jos jihar Plateau lokacin da wasu matasa dauke da bom din a kan babur yayi bindiga.

‘Yan sanda a birnin Jos, jihar Plateau Nigeria, sun bada rahoton kara samun fashewar bom a Jos jihar Plateau lokacin da wasu matasa dauke da bom din a kan babur yayi bindiga, anji kwamishinan ‘yan sandan jihar Plateau Abdulrahman Akano yana bayyanawa manema labarai cewa bom din ya tashi ne a dai dai lokacin da matasan ke dauke dashi suna sintiri a kan babur a unguwannin birnin Jos inda Musulmi da Kirista ke yawaita baiwa hamata iska.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa yau lahadi da safe ne fashewar ta afku a kusa da wata mujami’ar birnin Jos. Jami’an tsaron Nigeria sun kakkafa shingaye domin hana mutane kaiwa da komawa a yankin, amma hayaki ya turnuke sararin samaniyar yankin. Ba’a sami rahoton wata jikkata ba. Birnin Jos ya jima yana fama da tashe-tashen hankula, kama dai bisa dalilai na rabon fili, ko ayyukan yi da kuma harkokin siyasa. Mutane da dama suna rasa rayukansu.

XS
SM
MD
LG