Gwamanatin APC mai mulki a jihar Bauchi ta zargi gwamatin da ta shude na PDP karkashin mulkin Malam Isa Yuguda da dulmiyar da kudaden gwamnatin jahar fiye da naira miliyan dubu dari da tamanin a tsawon shekaru takwas da ta yi mulki a jihar Bauchin.
Shugaban kwamitin karbo kayayyakin gwamnatin jihar Bauchin da aka dauka ba bisa ka’ida ba Air komodo mai ritaya Ahmed Tijjani Baba Gamawa ya bayyana hakan a rahoton kwamitin da ya gabatar wa gwanan Bauchin Barrister Ahmed Abdullahi Abubakar.
Amma kakakin tsohuwar gwamantin Malam Isa ya ce babu sisin kwabon da aka kashe ba tare da samun izini ba; hasali ma kwamitin bai gayyaci wani jami’in tsohuwar gwamnatin domin jin ba’asi ba.
Ga wakilinmu Abdulwahab Muhammad da cikakken rahoton: