Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohon Shugaban Chadi Hissene Hare Ya Gurfana Gaban Kotu a Senegal


 Hissène Habré tsohon shugaban Chadi da ake zarginsa da yiwa dubban mutane kisan gilla
Hissène Habré tsohon shugaban Chadi da ake zarginsa da yiwa dubban mutane kisan gilla

Wata kotu ta musamman a Senegal, ta fara sauraren karar tsohon shugaban kasar Chadi, Hissene Habre, wanda ake tuhuma da aikata laifukan yaki da suka shafi cin zarafin bil adama.

A baya, Mr. Habre, ,mai shekaru 72 da kuma lauyansa, sun yi watsi da tuhumar kotun, suna masu cewa kotun ba ta bin ka’ida, saboda haka ba za su shiga cikin karar ba.

Amma a yau Litinin, Habre ya halaraci zaman kotun, bayan da hukumomi suka tilasta masa gurfana a gaban kotun.

An dai kafa kotun ne bisa wata yarjejeniyar da kasashen Tarayyar Afrika suka kulla, za kuma ta saurari bahasi daga shaidu 100 a wannan shari’a da ake sa ran za a kwashe watannin da dama ana yi.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama da wata kungiyar tabbatar da adalci a kasar Chadi, suna zargin Habre da laifin hanu a kisan da akawa fiye da mutane dubu 40 da ake dangantawa da siyasa, da azabtarwa a lokacin da ya ke mulki. Habre ya shugabanci Chadi a shekarun 1982 da 1990, inda daga baya shugaba mai ci na yanzu Idriss Deby ya hambarar da gwamnatinsa.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG