Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wai Jonathan Ya Mance da Yara 'Yan Matan Chibok ne


Shugaban Najeriya Jonathan ya sadu da wasu ‘yan makarantan mata da suka kubuta daga ‘yan Boko Haram 22, ga Yuli 2014.
Shugaban Najeriya Jonathan ya sadu da wasu ‘yan makarantan mata da suka kubuta daga ‘yan Boko Haram 22, ga Yuli 2014.

Yau kimanin wata shida Kenan da ‘yan matan makarantar Chibok suka bace, amma haryanzu babu wani labari.

Yau kimanin wata shida Kenan da ‘yan matan makarantar Chibok suka bace, amma haryanzu babu wani labari. Hajiya Fatima Abba Kaka wata jigo a kungiyar adawo muna da ‘yan matanmu wadda a turance ake cewa (Bring Back Our Girls) tayi kari haske dangane da wannan tattaki da zasuyi a yau don nuna ma duniya cewar lallai gwamnari Najeriya yakamata tayi kokari wajen gannin da kwato wadannan ‘yan matan.

Ta kara da cewar a wannan tattakin suna da bukatar yima shugan kasa tambayiyi wadanda suka hada da maganar ‘yan matan da aka sace da kuma wasu abubuwa da suka shafi harkar tsaro a kasar baki daya.

A cewar ta Hajiya Fatima akwai wasu yara da suka kai kamar 57 wadannada suka tsero daga hannun ‘yan ta’addar, ayanzu kuma akwai kimanin ‘yan mata 219 wadanda suke hannun ‘yan ta’addar. Ta kuma ce basu da ranar dena wannan tattaki har sai randa aka dawo da suran yaran.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:47 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG